Abban Sojoji Takun Karshe Book 3

𝔹𝕠𝕤𝕤 𝔹𝕒𝕥𝕦𝕣𝕖💋


 _💋The father Of Soldiers💋_



          *🔥TAKUN ƘARSHE🔥*

 Tsayawa abu tayi cike da mamaki take kallon ƙopar toilet din,don taji lokacin da aka banko ƙopar da ƙarfi aka rufeta,bata kawo komai aranta ba,tuni sun kammala breakfast din,jikinta ne baiyi mata daɗi,shine tashigo ɗakin  don tayi wanka kota jin daɗin jikin nata,


Hankalin jahad ba ƙaramin tashi yayi ba,duk tabi ta ruɗe baiwar Allah,junaid kuwa,koda suka faɗa toilet ɗin,wata irin zufa ce ke kartowa a kan fuskar kowannansu,sun ƙurawa juna ido,

  Muryarshi na kerma Yace"Jahad,dan Allah ki taimaka,ki fiddani daga cikin toilet ɗin nan,wlh idan oummanku ta ganmu atare zata sa a fasa bani auranki ne,"

  Muryarta tamkar zatayi kuka tace"Ya kakeso inyi junaid!duk laifinka ne,nayi maka magiya akan ka tafi amma kaƙi tafiya,yanzu duk wanda ya ganmu cikin toilet atare a irin wannan yanayin me kake tunanin zaiyi tsammani"?

  Tayi tambayar tana kallonshi,fuskarshi duk a hargitse,sai faman cizon yatsanshi yake yi,

  "Jahad na shiga ukuna,Wayyo Allah.....'

Bai kai ƙarshen maganar ba,ta sanya tafin hannunta,ta toshe mashi bakinshi,

  Cikin raɗa tace"Kayi shiru,kada agane cewa akwai mutun a toilet ɗin,"

  Shiru su kayi,yayin da suka ƙurawa junansu ido,lumshe idanuwanta ta ɗanyi batare data buɗesu ba,ba zato ba tsammani,taji ya faɗa mata,sosai ya qanqameta,hankalinta ya ƙara tashi,aruɗe ta shiga faɗin"junaid wai menene haka?wlh zanyi ihu kowa yaji muna acikin toilet ɗin nan,"

  "Jahad tsoro nake ji,dan Allah ki barni a haka,bazan ta6aki ba,"yana magana yana ƙara matseta ajikinshi,tarasa yaya zatayi dashi,ga Oumma acikin ɗakin,

  Batayi aune ba,taji yana goga lips ɗinshi saitin nipple dinta,kokarin kamawa yakeyi,A firgice jahad ta soma kiciniyar kwace shi,yaƙi sakinta,Ya ƙanƙameta yana faɗin"Wai menene haka jahad,so kika asirin mun ya tonu,

  A ƙule tace"bana son iskanci junaid,bazaka iya hakuri a ɗaura auran ba,"

  Da buɗar bakinsa sai cewa yayi"ae an biya sadaki,tun yanzu mu fara practicing," haushine ya isheta,saboda ƙarya yake yi,ba'a biya sadaki ba,Yana fakewa da hakan don ya samu tadinga yi mashi biyayya,

  Gartsa mashi cizo tayi asaman kafaɗarshi,abunka ga shagwa6a66en,Ya fasa ƙara tare da faɗin"Wayyo Allahna,Ta cije ni,"a gigice Jahad ta toshe mashi bakinta,ta janyoshi ta rungume don ta samu yayi shiru,


Abu dake acikin ɗakin,Abun ya ɗaure mata kai,domin kuwa tajiyo muryar mutun acikin toilet ɗin,bakin ƙopar ta nufa,ta ɗan tsaya tare da sanya hannu ta ƙwanƙwasa ƙopar"akwai mutun"

Gabansu ne ya faɗi,tuni ido ya raina fata,

"Junaid mun shiga uku,"tayi maganar,idanuwanta cike ta da kwalla 

  "Wai bakowa ne"?oumma ta ƙarayin tambayar,junaid yayi shiru ya lafe a ƙirjinta,jikinshi sai kerma yake yi ga tsoro ga iskanci cike dakai,

  Muryarshi na kerma yace"Jahad,kice mata kece,"

Jin haka yasa jahad ta ɗanyi gyaran murya,

  Ajiyar zuciya abu ta sauke tare da cewa"Lafiya naji kina ihu"?tayi maganar don ta gane wacece,

  Ƙasa ƙasa da murya jahad tace"Lafiyalou oumma,na sanya ruwan zafine,ban surka dakyau ba,"

  Jinjina kai abu tayi"ki ƙara surkashi mana,"

  "To oumma,"


Juyawa abu tayi maimakon ta fita daga ɗakin,Sai ta zauna gefen gadonsu,Tana jiran jahad ta fito itama ta shiga toilet ɗin tayi wanka 

  Hannu tasa ta 6an6are junaid daga jikinta,hannu yasa tare da dafe cikinshi,ya ɗan ɗago da dara daran idanuwanshi yana kallonta,zuba mashi ido tayi tana kallonshi,

  Kamar wani ɗan iska,Ya kashe mata ido ɗaya,tare da zuro harshen shi yana lasar gefen le6ensa,

  Abun ya bata haushi,jarabar junaid tafi ƙarfinta,ita duk a tunaninta yayi hankali tunda an rabashi da sihirin jikinshi ashe dama can tunfil azal,Ɗan iskan kanshi ne,

  Harara ta wurga mashi,tare da cewa"Wlh zan fasa auren,"

Bubbuga ƙafarshi ya ɗanyi,Ashagwaye yace"wlh da nayi maki lalata,kinga dole ki amince ayi auran,"

  Har sai da gabanta ya faɗi jin abunda yace,hankali atashe take kallonshi"nashiga uku junaid'

 

  Lamarin shi ya fara bata tsoro,ƙura ido tayi tana kallonshi,jiki asanyaye tace"Junaid,kana shaye shaye,"

  Girgiza kai yayi"wlh ko taba ban ta6a sha ba,"

  

Abu dake zaune gefen gadon tana jiran fitowar jahad,kunnuwanta suna jiyo mata ƙusƙus acikin toilet din,

  "Jahad,surutun me nake ji acikin toilet ɗin nan,ke da waye"?

  Aruɗe tace"babu kowa oumma,"jinjina kai abu tayi"kiyi sauri ki fito inaso in shiga,"

  Rass taji gabanta ya faɗi,amarairaice ta kalli junaid"Ya zamuyi,"

  "Nima kaina bansani ba jahad,pls ki nema mana mafita,"

  Shiru su kayi na wani lokaci,can taga yana nannaɗe jallabiyar jikinshi,tayi tunanin wata dabara zaiyi hada saurin cewa"Junaid,ka gano mana mafita ne"

  Batare daya kalleta ba,yace"fitsarine ya matse ni.....'

Tunkan yakai ƙarshen maganar,tayi hanzarin buge hannunshi"ashe baka da hankali,agabana zakayi,"

  "To sai me,wlh ya matse ni,in ba so kike inyi a wando ba,"zuba mashi ido tayi tana kallon ikon Allah,

  Ganin yana kokarin xame short ɗin ya curo abunshi yasa tace"Nashiga uku"!da ƙarfi tayi maganar,Abu dake zaune a ɗakin a firgice ta mike ta nufi toilet ɗin tana faman kwala mata kira"Jahad lafiyarki kuwa?wai me ke farune?tun ɗazu nake ta jin surutu acikin toilet ɗin nan,Zaman me kikeyi ne,Ya isa ace kin fito,"

  Hankali atashe Jahad tace"Babu komai oumma,Yanzu zan fito,kan famfo ne ya lalace,ruwa duk ya fallatsarmin,Shiyasa kika ji ina  magana,Yanzu zan gyara shi,ba wuya,"

Jinjina kai abu tayi"ok ina jiranki,"komawa tayi gefen gadon ta zauna tana jiran fitowarta,


  "Dan Allah junaid,kada kayi fitsarin nan,"a ƙule yace"ji wani ikon Allah,Nace dole saikin kalleni ne,ki juya baya mana,wlh sai nayi,"da sauri ta juya mashi baya,ta kifa kanta da bango,tana jin sautin fitar fitsarinshi,abun ya bata mamaki,kwata kwata junaid baida kunya,bata ta6a tunanin haka yake ba,tabbas zata sha wahala a hannunshi,don ba ƙaramin jarababbe bane,


Kwankwasa ƙopar ɗakin akayi,da sauri abu ta miƙe ta nufi ƙopar tana tambayar wanene,daga waje akace"Mommyn junaid ce,"hannu tasa ta buɗe mata ƙopar fuskarta ɗauke da murmushi,gaisawa suka fara yi kafin mommy tace"bansani ba ko Azeema ta sanar maki game da tafiyarmu dubai,"

  Girgiza kai abu tayi'a'a bata sanar dani komai ba,"

  Mommy tace"Inaji ta mantane,Dama zamuje haɗo lefen yaran nan ne,shine muka yanke shawarar zuwa can don muyi masu siyayya,amma kafin nan zamu fara zuwa kasuwa mu fara sayen wasu kayan anan,"

  Murmushi xainab ta saki"masha Allah,naji daɗi sosai,Allah yakaimu lafiya,"

  "Ameen ameen,"har mommy ta juya ta kuma cewa"oh na mata,Ya jikin Sehrish?tun a kitchen naso na tambayeki,Nayi tunanin ma idan nazo nan,zan sameta,"

  "A'a,suna a ɗayan ɗakin,Nima yanzu nake tunanin zuwa na duba jikinta,Ya jikin fawan?


  Mommy tace"da sauƙi sosai,Yanzu bai cika son fitowa waje ba,kullum yana ƙunshe a ɗakinshi,

   A ƙarshe abu tabi mommy suka tafi duba jikin sehrish,dana Fawan,'

  


Su jahad dake ƙumshe cikin toilet suna jin fitarsu,a hanzarce suka buɗe toilet ɗin,cikin sanɗa junaid ya lalla6a ya fuce daga ɗakin,Cikin sa'a bai ci karo da kowa ba,


Ajiyar zuciya jahad ta sauke,shaf shaf ta ɗauko kaya cikin wardrobe ta zura ajikinta,


*Boss Bature* 


*Reeshraf*


Sannu a hankali bacci ya ɗaukesu,rungume da juna,tamkar zai mayar da ita cikin cikinshi,a Lokacin da Mommy azeema tazo part din nashi,sallama ta fara yi shiru ba'a amsa mata ba,ranta ya bata cewa ko suna a cikin bedroom ne,Shiga cikin palourn tayi babu kowa,kaitsaye ta nufi wurin sofas ɗin,A saman table ta sauke masu trayn,yanke shawarar zuwa tadasu tayi,can kuma tayi tunanin yiwa omar magana,Ya kira shi a waya,don ya sanar mashi an kawo masu breakfast,


Sun yi nisa acikin baccinsu,wayar Sgr dake ajiye saman side drawer ta soma ringing,a hankali ya buɗe idanuwanshi masu ɗauke da bacci don bai ishe shi ba,akan fuskar sehrish ya saukesu,zuba mata ido yayi yana kallonta,sosai ta shige mashi,ta ƙanƙameshi,sai jan numfashi take yi,lumshe idanuwanshi yayi tare dakai hannu ya shafa sumar kanta,kafin ya manna mata kiss asaman forehead ɗinta,

  "I love u.....'ya furta ƙasa ƙasa da muryarshi,har kiran yayi rejecting wani kiran Ya kuma shigowa,Hannu ya miƙa saman drawer ɗin ya ɗauki wayar,tare da duba sunan mai kiran nashi,Omar ne,picking call ɗin yayi tare da kara wayar a kunnashi,

  "How are u my own bro,"

Muryarshi a kasalance yace"Am ok,ya kake?

  "Lafiya lou,jiya banji ya kuka ƙare da mutuniyar taka ba,"

Murmushi sgr ya saki,ɗayan hannunshi na acikin sumar sehrish yana wasa da ita yace"nasan duk kai ka shirya wannan,bansan da wasu kalmomi zanyi amfani ba wurin gode maka,

  Omar yace"ae ba komai,duk yiwa kaine,"

  "Tana tare dani,na samu kwanciyar hankali,yanzu haka ma kiran wayarka ne ya tashe ni,"

  Cike da zolaya Omar yace"Ya maganar tafiya U.s ɗin?ɗazu nazo part ɗinka,na samu trolley ɗinka ajiye,"

   "Ka fara ko"?

Dariya omar yayi"Nifa nayi tunanin yanzu haka jirginka ya sauka los angeles,"

   dariya Sgr ya ɗanyi,kafin yace"don't worry ur self,tunda na samu abunda nakeso,Very soon zamu tafi,"

  "Kada na takura maka,naga jiya bakaci abincin kirki ba,Ga break fast nan a palour an ajiye maku,kaida Babynka,"

  Ƙayataccen murmushi sgr ya saki tare da cewa"thank u Omar,"

  "Aunty azeema yakamata kayiwa godiya,duk ita ta shirya wannan,"acewar Omar,

  "Okey,zanje na same ta,"ya ambaci hakan yayin da hannunshi ke asaman wuyan sehrish,yana shafa shi,laushin skin ɗinta ba ƙaramin fusgarshi yake yi ba,

  "Sai anjima,but karka manta,kuyi feeding ɗin juna,hakan yana ƙara danƙon soyayya,"ya ƙarasa maganar muryarshi da alamun dariya yayi rejecting kiran,"yaji daɗin shawarar Omar sosai,don kuwa yana cikin tsarinshi,

  Ajiye wayar yayi saman drawer ɗin,a hankali ya matsar da fuskarshi saitin fuskar sehrish,saitin kunnanta yakai bakinsa,cikin raɗa ya ambaci sunanta"Reesh,can u hear me"?

  Shiru bata  Motsa ba,hannunshi ya sanya yana ɗan shafa bayanta,yaci gaba da ambaton sunanta cikin raɗa,har sai da Sehrish ta fara mutsu mutsu zata farka,tukunna ya janye kanshi daga saitin nata,

Biji biji ta fara ganinshi lokacin da take ƙoƙarin buɗe idanuwanta,ya tasa ta gaba yana kallonta,lips ɗinta duk sun bushe,still akwai jirwayen hawaye akan fuskarta,

   A hankali ta ambaci sunan shi"Ya rafayet,are u with me,"

  Shafa gefen fuskarta yayi"My wife,am sorry nayi disturbing dinki ko?na katse maki bacci"?

  Lumshe idanuwanta ta ɗanyi sun marairaice,

  "I know you're feeling hungry,that's why na tashe ki,"ya ƙarasa maganar,tare da kai hannu ya shafi cikinta,

  A hankali ta furta"Ina jin yunwa sosai,amma nafi buƙatar yin wanka,jikina duk babu daɗi,"yadda take magana tana ɗan yamutsa fuskarta,ba ƙaramin yanayi take jefashi ba,daurewa kawai yake yi,

  Miƙewa sukayi zaune saman gadon ganin tana ƙoƙarin ɗaukar hijab ɗinta yasa shi yin saurin cewa"Ba anan zaki yi ba"?

  Jinjina mashi kai tayi alamar eh,ɗaure fuskarshi ya ɗanyi alamar baiji daɗin maganarba,

  "Why ba zaki yi using da toilet ɗina ba,"?

"Idan kanaso,Sai nayi,"

Ta6a bakinshi ya ɗanyi"Sai inaso"?

  Girgiza kai tayi"Am Sorry,"

Ta ambaci hakan tare da saukowa daga saman gadon ta nufi toilet dinshi,ji yake tamkar yabita yayi mata wankan,amma yana jin shakkar ta6ata yanzu gudun kada a koma yar gidan jiya,ta burkice mashi tace Jikinta yake so,


Shiga toilet ɗin sehrish tayi tare da jan ƙopar ta rufe,saukowa sgr yayi daga saman gadon ya dawo bakin ƙopar toilet ɗin,ya jinginar da kanshi,don ya dinga jin motsinta,


Yana jiyo sautinta tana fadin"Assh..wash,"kamar ya faɗa toilet ɗin ya taimaka mata tayi wankan haka yake ji,


After some muninutes yaji motsinta a bakin ƙopar,komawa yayi gefen gadon ya zauna,yana jiranta,a hankali ta buɗe ƙopar,ta zuro ƙafarta kafin ta ƙarasa fitowa daga ciki,hannunta ruƙe da rigarta,skirt ɗin tajashi har saman ƙirjinta,gashin kanta duk ya rufe mata bayanta da  gefen fuskarta,natsuwa yayi yana kallonta batare da ƙiftawa ba,

   Tunda ta ɗago suka haɗa ido dashi,tayi saurin kawar da idonta,wani irin nauyinshi taji,


"Zan jiraki a palour,idan kin kammala shiryawa ki same ni acan,"

  Amsa mashi da toh,kafin Ya miƙe ya fuce daga ɗaikin,zubawa mirror ɗin ido tayi ganin babu glass ajikinshi,bata kawo komai aranta ba,mayukanshi na jiki masu ƙamshi tashiga shafe jikinta dasu,hada turarenshi ta fesa,bayan ta mayar da rigarta,sai da ta fara ɗaukar hijab dinta ta zurata,tukunna ta fito daga ɗakin,A saman Sofa ta same shi,ya jingina bayanshi jikinta,yayin da idanuwanshi ke a lumshe,a tsanake ta samu wuri gefenshi ta zauna,kafin ta ambaci sunanshi cikin sanyin murya"Yaya rafayet,"

  Buɗe idanuwanshi ya ɗanyi a hankali yana kallonta"har kin kammala,"ɗaga mashi kai tayi alamar eh,

  Yana ƙoƙarin kai hannu yayi serving dinsu tayi saurin rigashi"Zan zuba mana,"wani irin kallon so suke bin juna dashi,zama su kayi gwanin ban shawa'a tana bashi abaki yana bata,atare suka ciyar da junansu,bayan sun kamala cin abinci,ta faɗa mashi cewa zata je ta canza kayan jikinta,tana ƙoƙarin miƙewa ya ruƙo hannunta,tare da janyota ta faɗo saman laps ɗinshi,matsa hancinshi yayi asaman suman kanta"when are u coming back"?yayi tambayar cikin sanyin murya,kafin ta bashi amsa ya kuma cewa"kona minti ɗaya kikayi nesa dani,zanyi missing ɗinki sosai,'gaba ɗaya ya kashe mata jikinta,sae faman sauke ajiyar zuciya take yi,hannayenta duka biyun suna a dafe dashi,

   "Zan dawo da anjima,"

"Promise me,"ya ambaci haka yayin da yake shafa sumar kanta da hannunshi,

  "Nayi maka alƙawari,"jinjina kanshi ya ɗanyi,Okey,zan zuba ido naga zuwanki,idan ma baki zo ba,Ni zanzo,don na baki maganinki"ba don yaso ba,ya saketa,ta mike tare da kai hannu ta ɗauki tray ɗin kayan abincin da suka kammala ci,a hankali take tafiya,yayin da ranta ke bata cewa yana kallonta,


Sai da takai bakin ƙopar,ta ɗan dakata dayin tafiyar,juyawa tayi don ta saci kallonshi,karaf suka haɗa ido dashi,murmushi ta sakar mashi,shima ya mayar mata da martanin murmushi na gefen fuska,dimple ɗinshi ya lotsa,juyawa tayi da sauri ta fuce daga ɗakin,


Tana tafiya tana tunaninshi sai kace ba yansu suka rabu dashi ba,tsananin ƙaunarshi take ji acikin zuciyarta,kitchen ta fara zuwa ta ajiye tray ɗin hannunta,kafin ta koma besdroom ɗinsu,kaitsaye ta faɗa saman gadon,yayin da idanuwanta ke kallon sama,A hankali ta furta"I luv u so much Ya rafayet,Mijina nakaina"


A 6angaren hosana kuwa,Lokacin da taje Kai ma Omar abinci,Cike da zumuɗi ta zabga sallama hannunta ruƙe da tray,sae faman zabga murmushi take yi,kamar wata zautacciya,kamar yadda ta saba shiga ɗakin shi ko sallama babu,a haka ta faɗa ciki sai da tashiga tukunna tayi sallamar daga baya"Assalamu Alaikum"a lokacin yana kwance saman gadonshi,hannunshi ruƙe da wayarshi,ɗagowa yayi tare da kallonta,wani irin kyau yaga tayi mashi,miƙewa yayi daga zaune yana kallonta batare da ƙyaftawar ido ba,gaba ɗaya ta tafi da imaninshi,ganin ya ƙura mata yasa ta ɗan turo baki tare da cewa"Ya omar,wai lafiya kake kallona,"

Ajiyar zuciya ya ɗan sauke tare da cewa"hosana,wa yayi maki kwalliya?

"Ni nayi abunda,"

"Amma dai,ni akayiwa kwalliyar ko"?

Murmushi ta ɗan saki tare da ɗaga mashi gira alamar Eh,

  Ba ƙaramin daɗi yaji ba"Ki kaimun abincin falo,Yanzu zo muci tare ,

  Da sauri ta juya,tana shiga ta sauke tray ɗin a saman table,jiki na rawa ta zura hannunta cikin bra,ta zaro paper din da jahad ta rubuta mata kalaman soyayya,

  Karantawa ta farayi don ta samu ta haddace wasu kafin ya fito,

  "Ya Omar,inasonka so irin wanda uwa keyi ma jaririnta,kaine mutun na farko dana ji ya kwanta mun araina,nakeson kasancewa dashi na har abada,A matsayin mijina uban ya'yana,"tana cikin karantawa Tajiyo mutsu mutsun fitowarshi,A ruɗe ta nannaɗe takardar ta turata acikin bra ɗinta,


Ƙarasowa cikin falon yayi,hannu yasa ya ɗauki tray ɗin data ajiye saman table ɗin,Ya sauke shi saman carpet don suji daɗin cin abincin atare,


"Bismillah,"yayi maganar yana nuna mata wuri,da sauri ta zauna tare da lanƙwashe ƙafafunta,kamar yarda shima yayi,da kanshi ya zuba masu abincin Yace mata"mu fara ko'maƙe mashi kafaɗa tayi"Ae ni naci ya omar,kaidai kaci,"gyaɗa kai yayi batare da yayi mata musu ba,Ya soma cin abincin,

  Yana kokarin cin abincin karaf suka hada ido da ita,dakatawa ya ɗanyi"Wannan kallon fa"?

  Ƙayataccen murmushi ta ɗan saki tare da cewa"Kai dai kawai kaci gaba da cin abincin ka,"jinjina kanshi ya ɗanyi kafin ya mayar da hankalinshi kan abincin dayake ci,

  Tunani ta shiga yi,Ta manta kalaman data haddace,ganin hankalinshi baya akanta,yasa tayi sauri tura hannu ta ɗauko takardar duk ta cukuikuye,jikinta har kerma yake yi wurin karantawa,bayan ta kammala ta ninke ta mayar,

  Murmushi ta ɗan saki kafin tace"Ya Omar"ɗagowa yayi tare da kallonta yana jiran jin me zatace

   "Kasan yadda nakeson kuwa"?tayi tambayar fuskarta babu alamun wasa,

  Girgiza kai Omar yayi"a'a saikin faɗa,"

"Inasonka sosai ya omar,irin son da uwa keyi ma ɗanta,banajin zan iya rayuwa da wani ɗa namiji in bakai ba......'

Saboda tsabar mamaki baisan lokacin daya saki cokalin hannunshi ba,ya fada cikin plate ɗin gabanshi,zuba mata ido yayi yana kallonta,

  "Kaine tauraron dake haska zuciyata,dakai nake kwana dakai nake tashi Ya omar,bani da burin daya wuce in mallake ka a matsayin mijina......."

  A sukwane marshal ke kallonta,abun ya ɗaure mashi kai,kamar an sanya mata radio sai zuba take yi,abu kamar na hankali,ganin ta kakare yasa ta ɗan dakata tare dacewa"masoyina meyasa kake kallona?kaci gaba da cin abincinka mana,ni kuma zan cigaba da faranta maka rai"

   Shiru yayi yana tunanin taya akai hosana ta iya kalamai masu daɗi na hankali,Sam bai yarda da ita ba,

  "Hosana miƙe tsaye,"yayi maganar yana yi mata nuni da hannunshi,miƙewa hosana tayi,tsaf ya shiga kallonta daga saman har kasa,don yana zargin kamar karantowa take yi,ganin baiga komai ba yasa shi cewa tayi tsalle,

  Ranta ya 6aci sosai,a kule tace"Ni bazanyi ba,"

  Murmushin gefen fuska omar ya saki,

  "Shikenan,koma ki zauna,sannan kuma ki cigaba da fadamun daɗaɗan kalaman nan,inajin daɗinsu,"

Murmushi ta saki,cike da zumuɗi ta koma ta zauna,tana kokarin kai hannu ta zaro takardar ya kafe ta da idanuwanshi,duk tabi ta susuce,

  Ashagwa6e tace"Ya omar wai menene haka?ka ƙuramun ido,kaci gaba da cin abincinka mana,"

Girgiza kai yayi"a'a,nafi jin daɗin kallonki,yayin da kike faɗamunsu,"da biyu Omar yayi mata haka,

  Shuri tayi tana ta faman mazurai,domin kuwa bata iya komai ba,

  "Am listening to u,My baby "yayi maganar yana kallonta,

  Haushi ya isheta,daƙyar ta cigaba da cewa"yakai bunsurun dake cin ciyawar zuciyata,"

  Waro ido waje Omar yayi"Hosana!ni ne bunsurun"?da sauri ta sanya tafin hannu ta toshe bakinta,tana girgiza mashi kanta"wlh Ya Omar su6ul dabaka nayi,ba haka nakeso nace ba,kaine ka tsare ni da idanuwanka,"

   Harara ya ɗan jefa mata,Hannu yakai tare da ɗaukar lemu ya tsiyayashi Acikin cup,kafin ya ɗago tayi saurin Zura hannu ta ciro paper ɗin,hannunta nata kerma ta shiga dubata,da sauri ta mayar cikin bra ɗin ta ajiye,tana faman mayar da numfashi kamar wadda tasha gudu,

   Ɗagowar da zaiyi A furgice Yace"hosana!kyankyaso....."tana jin haka ta miƙe a ruɗe tana kakka6e jikinta,hada kuka nan take takardar da take ta faman 6oyo ta faɗo ƙasa a cukuikuye,tuntsirewa Omar yayi da dariya,hada dafe cikinshi,ya hasala ta sosai,Ta bubbuga ƙafarta,tare da fashewa da wani sabon kukan da gudu ta nufi hanyar fita daga falon tana kuka,miƙewa yayi da sauri yabi bayanta,har ya samu ya ruƙota tare da jangota jikinshi ya rungumeta,Yana ɗan bubbuga bayanta"Am sorry,banso na 6ata maki rai ba,nasan kinyi ne donki faranta mun raina,"


*Boss Bature*


A 6angaren Amrish kuwa,Har kusan one hour tana zaman jiran Kanal Yousouf,tuni ta jima da kammala Cin abincin,ta mayar da plate ɗin kitchen,A saman doguwar sofa ta kwanta tana jiran zuwanshi,har bacci ya ɗauketa,wuraren ƙarfe ɗaya da rabi,Motar shi ta ƙaraso bakin gate ɗin gidan,Yana yin horn baba mai gadi ya buɗe mashi,A mutunce suka gaisa da junansu,saboda ya ganeshi sosai,kuma yousouf yayi mashi bayanin zuwanshi,Bayan ya buɗe mashi gate ɗin ya wuce da motar cikin gidan,parking ɗinta yayi,kafin Ya fito ya nufi cikin gidan,A ƙopar shiga falon Ya tsaya yana zabga sallama shiru ba'a amsa mashi ba,kusan sau biyar,A karshe ya yanke shawarar shiga ciki,Da sallama abakinshi ya shiga falon,Tunkafin ya ƙarasa ciki ya hango Amrish,kwance tana bacci,gaba daya mayafinta ya zame ƙasa,tsayawa yayi yana kallon kitson kalabar dake akanta,manya manya,tayi mata kyau,baisan ta yarda zai tashe ta,Tunawa da makullin motar hannunshi Yasa shi yin dabarar girgiza key din saitin kunnanta,Sautinne Ya farkar da amrish daga bacci,mutsu mutsu ta fara tana kokarin buɗe idanuwanta,duk bata Lura dashi ba,har ta miƙe tsaye ta Sauko da ƙafafuwanta  ƙasa,Ta ɗaga hannayenta tana yin miƙa,Da sauri Yousouf Ya kawar da idanuwanshi,ganin yadda ƙirjinta ya fito sosai,

  Sai daga baya ta lura dashi,da sauri Ta ɗauko mayafinta,ta rufe kanta dashi,

  "Yaya yousouf,ka dawo,"

  Batare daya kalleta ba yace"Am sorry,na barki kina ta jirana,wani uzirine ya ruƙe.ni"

  "Babu komai,"ta ambaci hakan tare da mikewa ta ruƙo trolley ɗin kayanta,Gaba yayi tabi bayanshi har suka isa motar,kowa ya shiga ya zauna kafin ya tashi motar,ya nufi hanyar gida dasu,yana driving suna fira da ita,


*Boss Bature*


*Amani*


Tana cikin gyara kitchen tajiyo muryar Jahan daga falo yana kwaɗa sallama,fuskarta ɗauke da murmushi ta tunkari falon,A zaune ta same su saman Sofa,su biyu sun ɗauki wankan suits,ba ƙaramin kyau su kayi ba,dama duk in jahan zai zo zance,Atare da Ayaan suke zuwa,kamar yadda suke twins komai atare suke yinshi,


"Yau kune a gidan namu,"tayi tambayar tare da samun wuri ta zauna tana fuskantarsu,

  Haɗa baki su kayi wurin gaisar da ita"Ina yini aunty,mun same ku lafiya"?

  "lafiyalou,Ya kuke?ya mutanan gidan naku?Ya jikin junaid da fawan"?

  Ayaan yace"Kowa yana cikin ƙoshin lafiya,marasa lafiya kuma jiki yayi kyau,". 

  "Masha Allah abu yayi kyau,"acewar amani,

  "Bari nakawo maku abunsha"da sauri suka haɗa baki wurin cewa"a'a,bama bukatar komai,"

  Dariya ta ɗanyi,ba ƙaramin burgeta suke yi ba,har magana ma wani lokacin in zasu yi atare suke yinta,

  Ta lura da jahan sai faman waige waige yakeyi,

  "Amal ko"?tayi tambayar fuskarta ɗauke da murmushi,

  Murmushin gefen fuska Jahan ya saki tare da cewa"eh,tana ina ne?naga banganta ba"

"Bari nakira maka ita,"miƙewa tayi tare da juyawa ta nufi upstairs,

  "am so eager to see her,nayi kewarta sosai,"jahan ne yayi maganar yayin da yake zaro wayarshi daga cikin aljihunshi,

  Ayaan yace"In ka kwantar da hankalinka,Cikin ƴan kwanakin nan za'a shafa fatihar auranku,idan yaso saika mayar da ita madubi kayi ta kallonta,"

Harararshi jahan yayi "oh kana nufin zan aureta ne,kawai don na ajiyeta,na zuba mata ido ina kallonta?kaima ka sani wlh,"

  Dariya ayaan yayi,kafin ya ƙara cewa wani abu,Amal ta sauko jikinta sanye da riga da skirt na material maroon colour,tasha uban makeup,

  Da sauri jahan ya sanya tafin hannunshi Ya rufe ma Ayaan fuska,wai don kada ya kalle mashi matarshi,

  Buge hannun Ayaan yayi yana fadin"Me yayi zafi?Bari na tashi na baku wuri,idan kun kammala Zancen ka kirani in dawo in ɗaukeka,"yana kai ƙarshen maganar ya miƙe tare da nufar ƙopar fita falon yana dariya,

  Ƙarasowa Amal tayi,Tana ƙokarin zama ya nuna mata laps ɗinshi wai tazo ta zauna asama,waro ido waje tayi tana girgiza mashi kai"a'a kunya nake ji idan aunty amani ta gani fa,"

  Zare mata ido yayi"Ina wasa dake?zaki zo ki zauna ko sai ranki ya 6aci,"sam babu wasa a fuskarshi,dama haka take fama dashi,baida kunya ko kaɗan,ita kuma kunya gareta sosai,kuma sam bai iya soyayya ba,yafi ƙwarewa a harkar romance,ta ko'ina jahan yafi ƙarfinta,lalla6awa kawai take yi dashi don tana sonshi,


"Ni bazan zauna asaman cinyarka ba,Amma zan zauna a gefenka,in kuma hakan baiyi maka ba,ni zan koma ciki"idanuwanta cike tab da kwalla tayi maganar,

  Sassauta muryashi yayi"its ok,don't cry nima wasa nake maki,zoki zauna,"gefenshi ta zauna ya tsareta da idanuwanshi,sae faman gyara mayafinta take yi,saboda kallon ƙurullan da yake yi mata,. 

  "Baki yi farin ciki da zuwana bane"cikin sanyin murya yayi mata maganar,

  "Yakamata ki saki jiki dani,nan bada jimawa ba,za'a ɗaura mana aure,ko baki sona ne"?

  Ƙasa kasa da murya tace"inasonka mana,"

"To meyasa ko kallona bakya yi"?

Shiru tayi tana wasa da yatsun hannunta,matsawa yayi tamkar zai shige mata,ruƙo hannayenta yayi cikin nashi,

  "Amal,"ta amsa mashi da na'am,

"Yakama ki koyi zama dani,tun yanzu in ba haka ba,zakisha wahalata,Kin cika kunya,ni kuma banason mace me kunya,its better ki cire kunyarki wurin nuna mun soyayya,kinji ko"?

  Ɗaga mashi kai tayi alamar eh,

Shafa gefen fuskarta yayi"faɗamun idan munyi aure,a first night ɗinmu,me zaki yi mun,"shiru amal tayi tana tunanin amsar da zata bashi,hasalima bata gane me yake nufi ba, 

  "Kinyi Shiru bakice komai ba"?

Cike da jin kunyarshi tace"Ni bansan me kake nufi ba,"

  Dai dai satin kunnanta yakai bakinsa tare da cewa"I mean...idan zamuyi sunnah,"

Still bata gane me yake nufi ba, 

"Ya jahan ni ban fahimce kaba,"

Takaicine ya isheshi,a ƙule yace"oh,kina nufin bakisan Komai ba?a haka zamuyi aure?that's impossible,"

Ganin yadda ya 6ata ranshi yasa tace"Am sorry,wlh bansan kan me kake magana ba,"

  "Gaskiya idan har kinason mu zauna lafiya dake,to ki koyi yadda zaki farantamun kinji ni ko"?

  Ɗaga mashi kai tayi alamar eh,

"Idan na tafi,kice ma Auntynki ta koya maki yadda zaki kwanta da mijinki,ina fata kinji ni"?

  Gaba ɗaya ta dabarbace,Amma tabbas bata gane me yake nufi ba,

  "Zan faɗa mata,"jinjina kanshi yayi yanzu naji magana......'ya jima a wurin Amal,kafin yayi masu sallama,ya kira ayaan ya ɗaukeshi suka koma gida,


Domin sauke cikakken Littafin danna nan 👇👇👇👇

Abban Sojoji Takun Karshe Complete

Post a Comment

0 Comments

Ads