kowanne bayanin nono munyishi abaya shiyasa bama bukatar kawo jerin kalolinsa da yanda kowanne yake amma zamu duba abunda yake saka nonon mace daya yafi daya girma wanda yake kaiwa wasu jin kunyar fita ko acikin gida ballantana wajen miji .
abu na farko shine kwanciya akan nono wanda wasu matan keyi lokacinda nonon suke kanana tayanda kwanciyarsu tafi yawa gefe daya hakan idan yayi yawa sai dayan ya kankance saboda kan samansa be samu sakewa ba .
sai kuma ciwo wato nono daya yayi ciwo wannan shima yana iya mayarda daya ya zama daya .
Karanta>>> Dalilan Dake Zawo Rashin Sha'awa Ga Mata
Abu na gaba kuma lokacinda mace ke shayarwa idan bata kula wajen bawa yaro nono shima daya zaifi daya domin idan yaro ya daina shan daya tofa dole wanda akesha din ya zama karami . sannan akwai halitta wanda wasu haka suke kafin su fara shayarwa daya zaifi daya amma daga bisani suna daidaita .
kota wacce hanya hakan ya faru ahankali zai koma daidai wasu sai bayan sun haifu sun yaye wasu kuma sai sun dage dashan kunun alkama dana albasa.
Karanta>>> Dalilan Dake Sawa Nonuwa Suke Zama Kanana
KUNUN ALKAMA
Alkamar ake samu sannan asoya gyada waken suya sai ahada ayi garinsu ana dama kunu anasha.
Karanta>>> Ingantaccen Matsi Da Bashi Da Illah
KUNUN ALBASA
Zaki yanyanka albasa din acikin ruwa sannan ki dora akan wuta saita dafu saiki tace kisaka garin gero da zuma da madara ko nono kinsha sau biyu kullum . wadannan duka me ciki batasha
0 Comments